Subscribe Us

header ads

Coronavirus: Gwamnatin Kaduna ta gargadi mazauna jihar.

Coronavirus: Gwamnatin Kaduna ta gargadi mazauna jihar.



Gwamnatin jihar Kaduna da ke Najeriya ta gargadi mazauna jihar cewa za ta hana su damar fita daga gidajensu kwata-kwata idan suka ci gaba da bijire wa dokar hana fita.
Muyiwa Adekeye, mai magana da yawun gwamnatin jihar, ya ambato mataimakiyar gwamnan Kaduna, Dr Hadiza Balarabe tana cewa gwamnati ta lura mutane suna bijire wa dokar ta hana fita.
A cewar mataimakiyar gwamnan, za a hana mutane damar da aka ba su ta fitowa tsakanin karfe uku na ranar ko wacce Talata zuwa Laraba domin sayen kayan abinci da sauran abubuwan bukata idan suka ci gaba da yin biris da dokar gwamnati.
Mutum biyar aka tabbatar sun kamu da coronavirus a Kaduna, ciki har da gwamnan jihar Nasir El-Rufai.

Post a Comment

0 Comments