Subscribe Us

header ads

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dawo Da ‘Yan Nijeriya Mazauna Kasar Chana




Shugaba Buhari zai dawo da 'yan Nijeriya mazauna kasar Chana.

Ofishin jakadancin Nijeriya da ke birnin Beijing a kasar China, ne ya fitar da sanarwar.

Ofishin ya ce, gwamnatin tarayya ta kammala shirye-shirye domin fara jigilar 'yan kasar nan mazauna can domin dawo da su gida Nijeriya.

A cewar ofishin daukar wannan mataki ya biyo bayan fitar wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta wanda ya nuna yadda hukumomi a birnin Guangzhou suka fatattaki wasu ‘yan kasuwar kasar nan da dalibai da ke karatu a can kasar ta China daga dakunan Otal dinsu.

Rahotanni sun ce birnin Guangzhou shine gari da al’ummar Afirka suka fi ziyarta domin gudanar da harkokinsu na kasuwanci a kasar ta China.

Ofishiɓ yace sakamakon wannan abu da akewa yan Kasar Nigeria zata kwaso yan kasar ta daga Chinan.

Post a Comment

0 Comments